IQNA

Muftin Kasar Tunisia Ya Ce Yin Azumi A Cikin Corona Na Bukatar Mahangar Likitoci

23:52 - April 15, 2020
Lambar Labari: 3484713
Tehran (IQNA) babban malami mai bayar da fatawa na kasar Tunisia ya bayyana cewa, batun azumi a cikin corona na bukatar mahangar likitoci kan tasirin hakan ga lafiyar jama’a.

Shaffin yada labarai na businessnews.com ya bayar da rahoton cewa, Shekh Usman Battikh babban malami mai bayar da fatawa na kasar Tunisia ya bayyana cewa, batun azumi a cikin lokacin da ake fama da corona, na bukatar nazarin masana kiwon lafiya.

Y ace a halin yanzu ba zai iya bayar da fatawa ba kan batun ba tare da yin shawara da kuma jin mahangar likitoci kan wannan lamari ba.

Ya kara da cewa, a zaman da za a yi gobe zai yanke matsaya bayan jin ta bakin masana kan harkokin lafiya, dangane da yadda tasirin corona yake ga mutane masu azumi.

 

3891826

 

captcha