Bayanin ya ci gaba da cewa wannan taro zai samu halartar malamai da kuma masana gami da sauran muminai, inda za agabatar da jawabai a kan matsayin wannan limami mai tsarki da kuma tarihin rayuwarsa mai albarka.
Daga cikin wadanda za su gabatar da jawabai da kuma bege ga Imam Ridha (AS) akwai sheikh Haidar Arab, da kuma Haji Abu Ali Algiyawi, wadanda dukkaninsu sanannun fuskoki wajen gabatar da irin wadannan jawabai a kan limamai masu tsarki.
Cibiyar ta alkauthar ta ce tana mika gayyata ga dukkanin masu sha'awar halartar wannan taro maza da mata, wanda zai fara daga karfe 19 na daren Juma'a, kuma za akebance wurin mata daban da kuma na maza daban.