Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a jiya ne aka gudanar da taro kan kan fina-finan kasar Iran da aka tarjama a cikin harsunan faransanci da kuma wasu yaruka na kasar Senegal a birnin.
A lokacin kaddamar da wadannan fina-finai an bayyana wannan aiki a matsayin mai matukar amfani, domin kuwa dukkanin fina-finan da aka gabatar suna magana ne a kan lamurra na tarihin muslunci.
Haka nan kuma wasu daga cikinsu suna bayani ne a kan lamura da suka shafi yanayin al’adu da zamantakewar jama’a.
Gwamnatin kasar Senegal ta yi na’am da wannan mataki wanda take kallonsa a matsayin wada zai kara habbaka alaka tsakanin al’ummomin kasashen biyu.